Yohanna 17:15-20
15
Ba addu’ata ba ce ka ɗauke su daga duniya ba, sai dai ka kāre su daga mugun nan.
16
Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne.
17
Ka tsarkake su ta wurin gaskiya; maganarka ce gaskiya.
18
Kamar yadda ka aiko ni cikin duniya, haka ni ma na aike su cikin duniya.
19
Saboda su ne na tsarkake kaina, domin su ma a tsarkake su da gaske.
20
“Addu’ata ba saboda masu bina kaɗai ba ne. Ina addu’a kuma saboda waɗanda za su gaskata da ni ta wurin maganarsu.
Settings