Tsallake zuwa abun ciki
Ayuba 4:7-11

Koyarwar sakamakon ayyuka

Ayuba 4:7-11
7
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci, ’ya’yan zakanya kuma sun watse.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options