Tsallake zuwa abun ciki
Ayuba 39:26-30

Gudun tsuntsayen farauta na ɗabi’a

Ayuba 39:26-30
26
“Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
27
Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
28
Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
29
Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
30
’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options