Ayuba 37:9-13
9
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Settings