Ayuba 26:5-13
5
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe.
7
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
Settings