Ayuba 15:14-16
14
“Mene ne mutum, har da zai zama da tsarki, ko kuma mace ta haife shi, har yă iya zama mai adalci?
15
In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
16
mutum fa, wanda yake da mugunta da lalacewa, wanda yake shan mugunta kamar ruwa!