Skip to content
Ayuba 13:1-12

Ayuba 13:1-12

1
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options