Ayuba 13:6-12
6
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Settings