Skip to content
Ayuba 13:13-19

Ayuba 13:13-19

13
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options