Skip to content
Hosiya 7:1-3

Hosiya 7:1-3

Cin Hanci da Rashawa a Cikin Isra’ila

1
a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje, ’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
2
amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
3
“Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.

Duba kuma

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Hosiya 7:13

    Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
    daga aya ta 1
  • Luka 12:2

    Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
    daga aya ta 2
  • Zabura 90:8

    Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
    daga aya ta 2
  • Hosiya 6:4

    “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
    daga aya ta 1
  • Mika 7:3

    Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
    daga aya ta 1
  • Mika 7:7

    Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
    daga aya ta 1
  • Amos 8:7

    Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
    daga aya ta 2
  • Irmiya 2:19

    Muguntarka za tă hukunta ka; jan bayanka zai tsawata maka. Sai ka lura ka kuma gane yaya mugu da kuma ɗaci suke a gare ka sa’ad da ka rabu da Ubangiji Allahnka kuma ba ka tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
    daga aya ta 2
  • Irmiya 14:10

    Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
    daga aya ta 2
  • Romawa 1:32

    Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.
    daga aya ta 3
  • Hosiya 4:2

    Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
    daga aya ta 1
  • Irmiya 9:2

    Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
    daga aya ta 1

Inda wannan ya faru

Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options