Tsallake zuwa abun ciki
Farawa 1:1-5

Ranar farko ta halitta

Farawa 1:1-5
1
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
4
Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5
Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options