Skip to content
Kolossiyawa 3:5-10

Kolossiyawa 3:5-10

5
Saboda haka, sai ku fid da duk wani abin da yake kawo sha’awa a zukatanku, fasikanci, ƙazanta, sha’awa, muguwar sha’awa, da kuma kwaɗayi wanda shi ma bautar gumaka ne.
6
Gama fushin Allah zai sauko a kan masu aikata waɗannan.
7
Dā kun yi waɗannan abubuwa, sa’ad da rayuwar tana cikin duniya mai wannan hali.
8
Amma yanzu dole ku raba kanku da dukan ire-iren abubuwan nan. Ku daina fushi, ku daina ƙiyayya da ƙeta. Ku bar ɓatan suna da kuma ƙazamar magana daga leɓunanku.
9
Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun tuɓe tsohon halinku tare da ayyukansa
10
kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options