Skip to content
2 Korintiyawa 11:16-21

2 Korintiyawa 11:16-21

16
Ina sāke faɗa, kada wani yă ɗauka ni wawa ne. Amma in kun ɗauke ni haka, to, sai ku karɓe ni kamar yadda kuke karɓan wawa, domin in ɗan in yi taƙama.
17
A wannan taƙamata ba na magana yadda Ubangiji zai yi ba ne, sai dai magana ce irin ta wawa.
18
Da yake mutane da yawa suna taƙama irin ta duniya, ni ma haka zan yi.
19
Ku kam kuna da wayo sosai, har kuna jimre wa wawaye da murna!
20
Gaskiyar ita ce, kuna haƙuri da duk wanda ya sa ku bauta ko ya cuce ku ko ya more ku ko ya nuna muku isa ko kuma ya mare ku a fuska.
21
Ina jin kunya in ce mun nuna kāsawa da ba mu yi waɗannan abubuwan ba! Abin da wani yake da ƙarfin hali yin taƙama a kai, shi ne ni ma nake ƙarfin hali yin taƙama a kai. Ina magana kamar wawa ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options