Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 90:12-17

Addu’ar neman hikima da jinƙai

Zabura 90:12-17
12
Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
13
Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
14
Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
15
Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
16
Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga ’ya’yansu.
17
Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options