Zabura 9:7-12
7
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
11
Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
12
Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
Settings