Zabura 9:7-10
7
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Settings