Skip to content
Zabura 9:1-10

Zabura 9:1-10

1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
2
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
3
Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
4
Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
5
Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
6
Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
7
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options