Zabura 86:1-3
1
Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
2
Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
3
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.