Skip to content
Zabura 77:1-6

Zabura 77:1-6

1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. Sela
4
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options