Skip to content
Zabura 45:10-15

Zabura 45:10-15

10
Ki saurara, ya ke diya, ki lura ku kuma kasa kunne, Ki manta da mutanenki da gidan mahaifinki.
11
Sarki ya cika da sha’awar kyanki; ki girmama shi, gama shi ne maigidanki.
12
Diyar Taya za tă zo da kyauta, mawadata za su nemi tagomashinki.
13
Gimbiya tana fada, kyakkyawa ce ainun; an saƙa rigarta da zaren zinariya.
14
Cikin riguna masu ado aka kai ta wurin sarki; abokanta budurwai suna biye da ita aka kuwa kawo su gare ka.
15
Aka bi da su cikin farin ciki da murna; suka shiga fadan sarki.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options