Zabura 39:7-11
7
“Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
8
Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
9
Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
10
Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
11
Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. Sela
Settings