Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 25:16-20

Zabura 25:16-20

16
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka ’yantar da ni daga wahalata.
18
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options