Zabura 122:1-4
1
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Settings