Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 119:137-144

TSADI: Adalcin Allah da Himmin Mai Zabura

Zabura 119:137-144
137
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options