Zabura 116:1-6
1
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai.
4
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Settings