Skip to content
Zabura 115:12-18

Zabura 115:12-18

12
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da ’ya’yanku.
15
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options