Zabura 114:1-5
1
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
Settings