Skip to content
Zabura 108:6-13

Zabura 108:6-13

6
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options