Zabura 106:24-27
24
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Settings