Zabura 106:19-23
19
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Settings