- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Ubangiji ya shirya hanya ta wurin Yusufu
Zabura 105:16-25
16
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya ’yantar da shi.
21
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Settings