Skip to content
Karin Magana 30:1-6

Karin Magana 30:1-6

1
Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
2
“Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
3
Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
4
Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
5
“Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
6
Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options