Tsallake zuwa abun ciki
Karin Magana 21:20-26

Himma, kamun kai da kasala

Karin Magana 21:20-26
20
A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
21
Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
22
Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
23
Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
24
Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
25
Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
26
Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options