Skip to content
Karin Magana 11:15-21

Karin Magana 11:15-21

15
Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
16
Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
17
Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
18
Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
19
Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
20
Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
21
Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options