Skip to content
Filibbiyawa 3:5-8

Filibbiyawa 3:5-8

5
an yi mini kaciya a rana ta takwas, asalina Isra’ila ne, na kabilar Benyamin, mutumin Ibraniyawa ɗan Ibraniyawa; bisa ga doka kuwa ni Bafarisiye ne;
6
wajen himma kuwa, ni mai tsananta wa ikkilisiya ne, wajen aikin adalci bisa ga hanyar doka, ni marar laifi ne.

Sanin Almasihu fiye da kome

7
Amma abin da dā ya zama mini riba yanzu, na ɗauka hasara ce saboda Kiristi.
8
Me kuma ya fi, na ɗauki dukan abubuwa hasara ne in aka kwatanta da mafificiyar girman sanin Kiristi Yesu Ubangijina, wanda saboda shi ne na yi hasarar kome. Na mai da su kayan wofi, domin in sami Kiristi

Nazarin nassin nan

Sharhi a kan nassin, ba aya ɗaya ba

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Irmiya 9:23

    Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
    daga aya ta 8
  • Irmiya 9:24

    amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
    daga aya ta 8
  • Luka 14:33

    Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
    daga aya ta 7
  • Mattiyu 16:26

    Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
    daga aya ta 7
  • Romawa 8:18

    A ganina, wuyar da muke sha a wannan lokaci ba su isa a kwatanta da ɗaukakar da za a bayyana a cikinmu ba.
    daga aya ta 8
  • Mattiyu 13:44

    “Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
    daga aya ta 7
  • Mattiyu 13:46

    Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
    daga aya ta 7
  • Ayyukan Manzanni 20:24

    Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
    daga aya ta 8
  • Filibbiyawa 3:7

    Amma abin da dā ya zama mini riba yanzu, na ɗauka hasara ce saboda Kiristi.
    daga aya ta 8
  • Luka 14:26

    “Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da ’ya’yansa, da ’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
    daga aya ta 7
  • Karin Magana 13:8

    Arzikin mutum zai iya kuɓutar da ransa, amma matalauci ba ya jin barazana.
    daga aya ta 7
  • Yohanna 17:3

    Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko.
    daga aya ta 8
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options