Skip to content
Ƙidaya 15:32-36

Ƙidaya 15:32-36

32
Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
33
Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
34
sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
35
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
36
Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options