Ƙidaya 15:32-34
32
Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
33
Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
34
sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.