Skip to content
Ƙidaya 13:3-16

Ƙidaya 13:3-16

3
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options