Ƙidaya 10:14-27
14
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
15
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
16
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
17
Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
18
Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
19
Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
20
Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
21
Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
22
Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
23
Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
24
Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
25
A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
26
Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
27
Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
Settings