Skip to content
Mattiyu 6:9-15

Mattiyu 6:9-15

9
“To, ga yadda ya kamata ku yi addu’a. “ ‘Ubanmu wanda yake cikin sama, a tsarkake sunanka,
10
mulkinka yă zo a aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a sama.
11
Ka ba mu yau abincin yininmu.
12
Ka gafarta mana laifofinmu, kamar yadda mu ma muke gafarta wa masu yin mana laifi.
13
Kada ka bari a kai mu cikin jarraba, amma ka cece mu daga mugun nan.’
14
Gama in kuna yafe wa mutane sa’ad da suka yi muku laifi, Ubanku da yake cikin sama ma zai gafarta muku.
15
Amma in ba kwa yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku ma ba zai gafarta muku zunubanku ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options