Skip to content
Mattiyu 5:43-48

Mattiyu 5:43-48

43
“Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka,ka kuma ƙi abokin gābanka.’
44
Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābankukuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a,
45
don ku zama ’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci.
46
In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba?
47
In kuwa kuna gai da ’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba?
48
Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options