Skip to content
Mattiyu 5:21-24

Mattiyu 5:21-24

21
“Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai;kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’
22
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta.
23
“Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci,
24
sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options