Mattiyu 26:1-5
1
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
2
“Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
3
Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
4
suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
5
Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
Settings