Mattiyu 23:1-7
1
Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
2
“Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
3
Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
4
Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
5
“Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
6
suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
7
suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
Settings