Skip to content
Mattiyu 22:41-46

Mattiyu 22:41-46

41
Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su,
42
“Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?” Suka amsa suka ce, “Ɗan Dawuda.”
43
Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,
44
“ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.” ’
45
To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?”
46
Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options