Skip to content
Mattiyu 11:7-15

Mattiyu 11:7-15

7
Sa’ad da almajiran Yohanna suke barin wurin, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna. “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
8
In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da riguna masu kyau ne? A’a, masu sa riguna masu kyau, ai, a fadan sarakuna suke.
9
To, me kuka je kallo ne? Annabi? I, ina gaya muku, ya ma fi annabi.
10
Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “ ‘Zan aiki ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka a gabanka.’
11
Gaskiya nake gaya muku. A cikin dukan waɗanda mata suka haifa, ba wani da ya taso da ya fi Yohanna Mai Baftisma girma; duk da haka mafi ƙanƙanta a mulkin sama ya fi shi girma.
12
Tun daga kwanakin Yohanna Mai Baftisma har yă zuwa yanzu, mulkin sama yana sha da ƙyar, fitanannu kuma sun kama mulkin sama sun riƙe gam.
13
Gama dukan Annabawa da kuma Doka sun yi ta annabci har yă zuwa kan Yohanna.
14
In kuna niyya ku yarda da wannan, to, shi ne Iliya da dā ma zai zo.
15
Duk mai kunnen ji, yă ji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options