Skip to content
Mattiyu 11:2-6

Mattiyu 11:2-6

2
Sa’ad da Yohanna Mai Baftisma ya ji a kurkuku abin da Kiristi yake yi, sai ya aiki almajiransa
3
su tambaye shi, “Kai ne wanda zai zo, ko kuwa mu sa ido ga wani?”
4
Yesu ya amsa ya ce, “Ku koma ku gaya wa Yohanna abin da kuka ji, kuka kuma gani.
5
Makafi suna gani, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin labari mai daɗi.
6
Mai albarka ne mutumin da bai yi tuntuɓe ba saboda ni.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options