Skip to content
Markus 6:7-11

Markus 6:7-11

7
Ya kira Sha Biyun nan wurinsa, ya aike su biyu-biyu, ya kuma ba su iko bisa mugayen ruhohi.
8
Ga dai umarnansa, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, sai dai sanda ba burodi, ba jaka, ba kuɗi a ɗamararku.
9
Ku sa takalma, amma ban da riga fiye da waɗanda kuka sa.
10
Duk sa’ad da kuka shiga wani gida, ku zauna nan sai kun bar garin.
11
In kuwa a wani wuri ba a karɓe ku, ba a kuwa saurare ku ba, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita, a matsayin shaida a kansu.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options