Markus 3:14-19
14
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
Settings