Tsallake zuwa abun ciki
Luka 4:14-19

Luka 4:14-19

14
Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
15
Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
16
Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
17
Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
18
“Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar ’yanci ga ’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da ’yanci ga waɗanda aka danne.
19
In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options